Insane
Africa Mobile Blog

Hotuna daga taron hadakar PDP, R-APC da ragowar jam'iyyu fiye da 30 domin fitar da dan takara guda



Jam’iyyar Adawa da PDP da wasu jam’iyyun Najeriya 33 su hadu a wani dakin taro dake Musa Yar Adua a Abuja domin saka hannu a kan yarjejeniyar yin aiki tare domin kwace mulki daga hannun jam’iyyar APC mai mulki.

Yayin taron nasu, jam’iyyun sun rattaba kan yarjejeniyar marawa dan takara guda baya da zai fafata da shugaba Buhari da zai yiwa jam’iyyar APC takara. Cikin jami’yyun da suka halarci taron akwai, SDP, NCP, ADC, da kuma jami’yyar adawa ta Labour.

Daga cikin jiga-jigan ‘yan siyasa da suka halarci wurin taron na yau akwai shugaban jam’iyyar PDP, Uche Secondus, tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, da Buba Galadima; shugaban sabuwar jam’iyyar R-APC da ta balle daga APC, da kuma jagoran nPDP, Kawu Baraje.
!-- -- Back to posts
This post has no comments - be the first one!